"Suna Neman Kassara Tinubu", Kungiyar Arewa Ta Soki Atiku da El Rufai Kan Ziyartar Buhari
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Katsina - Kungiyar Arewa Think Tank ta caccaki ƴan siyasa da ke ziyartar Muhammadu Buhari a jihar Katsina.
Kungiyar ta ce ba ta ki ƴan siyasa su kai wa junansu ziyara ba amma wannan cike yake da munafurci da kuma cin amana.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Kwamred Mohammed Aliyu Yakubu ya fitar, cewar The Nation.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kungiyar ta gargadi masu ziyarar domin neman shawara kan zaben 2027 da su yi hakuri babu wuri a fadar shugaban ƙasa.
Ta bayyana cewa babu wanda zai samu wuri har sai Shugaba Bola Tinubu ya kammala wa'adinsa na shekaru takwas a kan mulki.
Wanna martani na zuwa ne bayan tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ziyarci Buhari a Daura.
Daga bisani, tsohon gwamnan Kaduna, Nasiru El-Rufai shi ma ya kai ziyarar wanda jama'a da dama ke hasashen duk a kan zaben 2027 ne.
"Ziyarar da wasu manyan ƴan siyasar Arewa suka kai wa Buhari duk a kan zaben 2027 domin yiwa Tinubu illa."
"Mun gano dan takarar shugaban kasaPDP, Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Kaduna, Nasiru El-Rufai sun kai masa ziyara a Daura."
"Ziyarar sallah aka kai a bayyane amma akwai makarkashiyar siyasa kan irin wannan yanayi ganin 2027 na tafe."
"Bai kamata tun yanzu masu kwadayin mulki daga Arewa su fara irin wannan shiri ba ganin cewa Tinubu shekara daya kawai ya yi a kan mulki."
- Arewa Think Tank
A wani labarin, kin ji cewa dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari gidansa da ke Daura.
Atiku ya kai ziyarar domin mika gaisuwar sallah ga tsohon shugaban kasar kammala wa'adinsa na shugabancin Najeriya.
Asali: Legit.ng