Me ya kamata iyayen yaran da ake cin zali a makaranta su yi?
Tun dai bayan da wani bidiyo ya fara waɗari a shafukan sada zumunta ranar Litinin na yadda wasu ɗalibai mata ke gaura wa wata ɗaliba mari, yayin da wani gungu kuma ke ɗaukar bidiyon, iyayen yara 'yan makaranta ke ta nuna damuwa dangane da al'amarin da neman yadda za su fahimci ana cin zalin 'ya'yan nasu.
Bisa kalaman da ke fitowa daga bidiyon, an fahimci cewa soyayya ce ta janyo rikicin, inda mai marin ke zargin wadda ake mari da ƙwace mata masoyi.
Bayan fitowar wannan bidiyo ne kuma sai wasu waɗanda suka fuskanci irin wannan cin zali su ma suka yi ta fito da bidiyo da hotunan cin zalin da suka fuskanta a makarantar.
To sai dai a wata sanarwa da makarantar mai suna Lead British School Abuja ta fitar, ta ce ta ga abin da ya faru kuma tana bincike domin tabbatar da ɗaukar matakin da ya dace.
To shin ko me ya kamata su kuma iyayen yaran da ake cin zali su yi?
BBC ta tattauna da Dakta Hauwa Ɓaɓura masaniya kan harkar karatun ƙananan da lafiyar ƙwaƙwalwarsu kuma mai bai wa gwamnan jihar Jigawa shawara kan ilmi matakin farko, dangane da abin da ya kamata iyayen yara su yi domin gano ana cin zalin 'ya'yansu.
Dakta Hauwa ta ce matakin farko na gane abin da yaronka ko yarinyarki ke ciki a makaranta shi ne jan su a jiki.
"Idan dai har uwa ba za ta ja ɗanta ko ƴarta a jiki ba to da wuya iyaye su fuskanci halin da 'ya'yan nasu ke ciki. Ka ga ba za ki taɓa fahimtar lokacin da ƴarka ko ƴarki take cikin walwala ko akasin haka." In ji dakta Hauwa.
To sai dai kasancewar a wannan bidiyon da ya bayyana, ɗaliban da abin ya shafa a makarantar kwana su ke a saboda haka bai zama lallai mahaifa su fahimci halin da suke ciki ba.
Amma dakta Hauwa ta ce "ba haka ba ne saboda idan dai har iyaye suna jan 'ya'yansu a jiki to ai zamani ya ba su damar yin waya da catin sannan kuma ai ana zuwa ziyara akai-akai kenan yaran za su sanar da su idan dai suka nemi bayani dangane da halin da suke ciki." In ji dakta Hauwa.
Dangane kuma da matakin da ya kamata mahaifi ya ɗauka bayan samun labarin cin zalin ɗa ko ƴarsa dakta Hauwa ta ce "duk abin da ya samu ɗanka ko ƴarka ka yi shiru to ka cuci wannan yaron ko yarinyar da ma sauran yaran da za su iya fuskantar irin wannan tsangwama a nan gaba.
Da zarar kun samu labari ko kuma kun fahimci hakan to a fara da ɗaukar matakan tuntuɓar makarantar idan kuma abin ya fi karfinsu sai a bi hanyoyin shari'a." A cewar dakta Hauwa.
Dakta Hauwa ta ƙara da gargaɗar makarantu cewa su ma da laifinsu sakamakon ko dai rashin bincike da sa ido ko kuma ɗauke kai daga abin da suke ganin bai taka kara ya karya ba.
"To amma idan iyaye suna zuwa su tunkari makarantun ko ma su ɗauki matakan shari'a to za ku ga makarantun suna ɗaukar matakan da suka dace. Sannan dole ne ita ma gwamnati ta saka idanu kan irin waɗannan makarantu." A ta bakin Dakta Hauwa.
Emmanuel Paul Asan, ƙwararen likita kan tunanin ɗan adam da ke aiki a asibitin Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi ya lissafa ire-iren cin zali.
Dakta Emmanuel Paul Asan ya ce cin zali na shafar ƙwaƙwalwar yaro ta fanni daban-daban. Sun hada da