Home Back

Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

leadership.ng 2024/8/23
Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Baffa Dan Agundi a matsayin sabon Darakta-Janar na cibiyar inganta aikin ta ƙasa. Baffa Dan Agundi ya taɓa yin aiki a matsayin shugaban masu rinjaye na Majalisar Dokoki ta Jihar Kano da kuma Babban Sakataren Kotun Manyan Laifuka ta Jihar Kano.

A cewar Ajuri Ngelale mai ba shugaba Tinubu sawara kan harkokin yada labarai, Shugaba Tinubu yana sa ran Baffa Dan Agundi zai nuna cikakken sadaukarwa da kishin ƙasa wajen inganta ayyukan cibiyar.

Wannan yana nufin samar da al’adar ingantaccen aiki da kuma ƙarfafa tunanin aiki don samun kyakkyawan sakamako da inganta rayuwa a Nijeriya.

Wasu daga cikin mukaman da Baffa Dan Agundi ya riƙe sun haɗa da; shugabancin hukumar KAROTA da hukumar haƙƙin masu sayayya ta Kano.

People are also reading