Home Back

Biyan Albashin Da Ƙungiyar Ƙwadago Ke Nema Na Iya Durƙusar Da Nijeriya

leadership.ng 2024/7/2
Mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale
Mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale

Fadar shugaban ƙasa ta nuna rashin amincewa da buƙatar ƙungiyar ƙwadago na neman ƙarin mafi ƙarancin albashi na ₦494,000, inda ta yi gargaɗin cewa hakan zai durƙusar da tattalin arzikin Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale ne ya bayyana irin illar da hakan zai iya haifarwa yayin wata hira a gidan Talabijin na TVC, yana mai jaddada cewa irin wannan ƙarawar zai tilastawa kananan ‘yan kasuwa da dama rufe, wanda hakan zai kara ta’azzara rashin aikin yi da tabarbarewar tattalin arziki.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale
Mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale

Ngelale ya ƙara da cewa shirin ƙarin albashin da ake shirin yi wanda ya ninka kusan sau 20 a matsayin mafi ƙarancin albashi a halin yanzu, zai ɗora wa ƙananan ƴan kasuwa wani nauyi da ba zai ɗore ba, wanda hakan zai haifar da rufewar kamfanoni da kuma asarar ayyukan yi.

Albashi

Ƙungiyoyin ƙwadagon Najeriya NLC da TUC sun fara yajin aikin sai baba-ta-gani a faɗin ƙasar sakamakon ƙin amincewar da kuɗin da gwamnatin tarayya ta ce zata biya na mafi ƙaranci ₦60,000.

People are also reading