'Yan Kasuwa Sun Faɗi Abin da Ya Jawo Tsadar Kayan Abinci, FCCPC Ta Kai Samame Onitsha
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Awka, Anambra - Jami'an hukumar FCCPC sun kai samame babbar kasuwar kayan abinci ta Oseokwodo, Onitsha kan tsadar da kayan abincin suka yi.
Sai dai 'yan kasuwar sun shaidawa jami'an gwamnatin tarayyar cewa rashin tsaro a fadin kasar ne ya jawo hauhawar farashin kayan.
Kodinetan shiyyar Kudu maso Gabas na hukumar FCCPC, Mista Jude Akonam ya ce sun kai samamen ne domin gano dalilin tsadar kayan, in ji rahoton Vanguard.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Mista Akonam ya ce za su sanarwa hukumomin da ya dace abin da binciken su ya gano domin daukar matakin da ya dace kan tsadar abincin.
Shugabannin 'yan kasuwar sun ce kasuwar Oseokwodo ta kasance wuri da jama'a ke sayen kayan abinci a cikin farashi mai rahusa.
Amma sun ce tashin farashin kayan abinci a kasuwar alama ce da ke nuni da cewa lamarin ya fi karfin 'yan kasuwar ne su ma.
Sakataren kungiyar OOMTU, Mista Onyekekwe Cyprian wanda ya bayyana kasuwar matsayin cibiyar hada-hadar kayan abinci ya Anambra, ya ce tsadar ba daga su bane.
Da yake alakanta lamarin ga matsalar tsaro, Mista Cyprian ya ce yanzu manoma na tsoron zuwa gonakinsu saboda 'yan bindiga da ke sace su, jaridar The Punch ta ruwaito.
Shugaban 'yan kasuwar ya ce sau tari ana tare manoma a gona ko a hanyar zuwa kai kaya kasuwa ko a hanyar dawowa ayi garkuwa da su.
Ya ce wannan dalilin ya sa yanzu kayan abinci ya yi ƙaranci a kasuwa, yayin da su 'yan kasuwar ne ke zuwa wajen manoman da kansu suna dauko kayan.
A wani labarin, mun ruwaito cewa 'yan kasuwar hatsi na jihar Kano sun karya farashin kayan abinci sakamakon tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasar.
Shugabannin kasuwar sun koka kan yadda kayan abincin ke tsada yayin da kuma ciniki yayi karanci a kasuwannin saboda rashin kuɗi a hannun jama'a.
Asali: Legit.ng