Rusau a Kasuwar Lagos: Zuciyar Dattijuwa Ta Buga, Ta Ce Ga Garinku Nan
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Lagos- An shiga takaici a jihar Lagos bayan zuciyar wata ‘yar kasuwa, Alhaja Iyabo ya buga, wanda ya yi sanadiyyar rasuwarta.
Zuciyar marigayiyar ya buga ne bayan ta tafka asara a rusau din da gwamnatin jihar Lagos ke yi a kasuwar Alaba Rago.
Daily Trust ta tattaro cewa baiwar Allah ta rasa akalla N50 da ta ajiye a asusunta dake cikin shagon da aka ruguje.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin jihar Lagos ta sanar da ‘yan kasuwar Alaba Rago cewa za ta fara rushe kasuwar, saboda haka su tashi.
Shugabannin kasuwar sun bayyana cewa gwamnati ta fara rushe kasuwar inda a yanzu aka tabbatar da rasa akalla N50b, kamar yadda Nairaland ta wallafa.
Daga cikin kayan da aka rasa a kasuwar akwai shinkafa, wake, da dabbobin ‘yan kasuwar ciki har da Alhaja Iyabo da ta rasa ranta.
Wasu daga ‘yan kasuwar Alaba Rago kamar shugaban masu sayar da shanu, Mallam Ibrahim Hamad Namari, ya ce babu wata sanarwa daga gwamnati kan fara rusau.
Ya ce an bawa wani bangare na kasuwar sanarwar cewa za a fara rusa, amma ba abayyana ainihin rana ko wuraren da za a rushe ba.
Mallam Ibrahim Hamad Namari, ya ce bayan sun samu labarin fara rusau suka dunguma kasuwar, inda suka tarar da dimbin asara.
A baya mun kawo muku labarin yadda wani maniyyacin aikin hajjin bana daga jihar Lagos, Idris Olosogbo ya riga mu gidan gaskiya bayan ya isa kasa mai tsarki.
Marigayin wanda ya rasu ne bayan ya dawo daga dawafi, kamar yadda babban sakataren hukumar jin dadin alhazan jihar Lagos Saheed Onipede ya shaida.
Asali: Legit.ng