Mafi Karancin Albashi: Na Kusa da Tinubu Ya Fadi Abinda Ya Kamata a Biya Ma'aikata
FCT, Abuja - Na kusa da shugaban ƙasa, Bola Tinubu, Daniel Bwala, ya bayyana mafi ƙarancin albashin da ya kamata gwamnati ta biya ma'aikata.
Daniel Bwala ya bayyana cewa kamata ya yi mafi ƙarancin albashin ma'aikatan Najeriya ya kasance N250,000.
Daniel Bwala ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da tashar TVC News kan yajin aikin da ƙungiyoyin ƙwadago suka fara.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ƙungiyoyin ƙwadagon sun shiga yajin aiki ne kan sabon mafi ƙarancin albashi da ƙarin kuɗin wutar lantarki ga masu amfani da rukunin 'Band A'.
A daren ranar Litinin, 3 ga watan Yunin 2024, gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ƙwadago sun cimma yarjejeniya kan sabon mafi ƙarancin albashi wanda zai wuce N60,000.
Daniel Bwala ya bayyana cewa N60,000 da gwamnati ta yi tayin za ta biya a matsayin mafi ƙarancin albashi ya yi kaɗan.
"Duba da hauhawar farashin kayan abinci da tsadar rayuwa a Najeriya, N60,000 ba za ta je ko'ina ba."
"Ko gwamnatin tarayya ta san da hakan. Ban tunanin duk wani mai cikakken hankali zai ce abin da ƴan ƙwadagon ke neman shirme ne. Aa abu ne da ya cancanta amma ba za a iya samar da shi ba."
"Ina tunanin ya kamata gwamnati ta ƙara abin da ta ce za ta biya. Ban tunanin gwamnati na cewa N60,000 shi ne ƙarshen abin da za ta iya biya."
"Idan aka tambayeni, a tunanina kamata ya yi mafi ƙarancin albashi ya kasance N250,000 a Najeriya. Amma idan kana tunanin haka ya dace amma ba kuɗin da za a iya biya, sai a yi haƙuri da abin da ya samu."
- Daniel Bwala
A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyoyin ƙwadagon Najeriya na NLC da TUC sun dakatar da yajin aikin sai baba ta gani da suka fara a ranar Litinin a faɗin ƙasar nan.
NLC da TUC sun tsagaita yajin aikin ne na mako ɗaya rak, a kokarin da suke yi na ganin su da gwamnatin tarayya an cimma matsaya kan mafi ƙarancin albashi.
Asali: Legit.ng