Home Back

NNPCL Ya Bayyana Ranar Da Matatar Man Fetur Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki

leadership.ng 2024/5/18
NNPCL Ya Bayyana Ranar Da Matatar Man Fetur Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki

Hukumar kula da kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) ta ce, za a kammala aikin gyaran matatar man fetur ta Kaduna (KRPC) a karshen shekarar 2024 bayan shafe shekaru a rufe saboda rashin kulawa.

Babban mai kula da matatar KRPC, Mustafa Sugungun ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a yayin ziyarar sa ido a matatar man da kwamitin ‘yan majalisar dattijai a karkashin jagorancin Sanata Ifeanyi Ubah suka kai matatar.

Ya bayyana cewa, matatar mai tace ganga 110,000 a kowace rana za ta fara aiki da kashi 60 cikin 100 nan da karshen shekara, yayin da ake sa ran za ta ci gaba zuwa kashi 100 na cikakken aiki daga baya.

Shugaban na KRPC ya bayyana cewa, aikin gyaran, wanda a halin yanzu ya kai kashi 40 cikin dari, ana sa ran kammala shi cikin wa’adin da aka kayyade.

People are also reading