Home Back

An tuhumi malamin addini a Kenya da ta'addanci

dw.com 2024/8/21
Fasto Paul Mackenzie a zaune a kotu
Fasto Paul Mackenzie a zaune a kotu da ke Mombasa na kasar Kenya

Mutumin da ya bayyana kansa a matsayin Pastor Paul Mackenzie, ya gurfana ne a wata kotun da ke birnin Mombasa, inda a bara Pastor Mackenzie ya ceda mabiyansa suna iya daina cin abinci har su mutu, domin zuwa su hadu da Yesu Kirista.

Malamin addinin na Kirista wanda ke da 'ya'ya bakwai da wasu abokan aikinsa mutum 90, ya musanta zargin aikata kisan kai da aka yi masa a kotu cikin watan Janairu.

Hukumomi a Kenya dai sun tilasta tono gawarwakin mutanen da suka mutu, domin binicke kan batun da ya yi matukar daukar hankalin duniya a baran.

People are also reading