Home Back

Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano

leadership.ng 2024/5/16
Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano

Hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, ta ce ta ceto mutane 12 da kadarori da kudinsu ya kai Naira miliyan 130 daga gobara 78 da suka faru a watan Maris a jihar.

Kakakin hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi ne, ya bayyana hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), a ranar Laraba a Kano.

Abdullahi, ya kuma ce mutane 10 ne suka mutu, yayin da gobarar da ta lalata kadarorin Naira miliyan 71.

“Mun samu kiran agaji 27 da wayar karya 11 daga mazauna jihar a tsawon watan Maris,” in ji shi.

Ya shawarci jama’a da su kasance masu kula da abubuwan da suka shafi wuta.

People are also reading