Home Back

Sanusi II vs Aminu Ado: ’Yan Najeriya Sun Yi Martani Bayan Hukuncin Kotu a Kano

legit.ng 2024/7/7
  • A yau Babbar Kotun Tarayya ta yi hukunci kan dambarwar masarautun jihar Kano tsakanin Sanusi II da Aminu Ado Bayero
  • Kotun ta rusa duka matakan da Gwamna Abba Kabir ya dauka bayan dokar rushe masarautun guda biyar da aka kirkira a 2019
  • Ƴan Najeriya da dama sun bayyana ra'ayoyinsu game da lamarin inda suka sha bamban kan yadda hukuncin ya kaya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - A yau Alhamis 20 ga watan Yunin 2024 Babbar Kotun Tarayya ta yi hukunci kan dambarwar sarautar Kano.

Kotun yayin hukuncin ta rushe matakin da Gwamna Abba Kabir ya dauka kan soke masarautn jihar guda biyar.

'Yan Najeriya sun bayyana ra'ayoyinsu kan hukuncin kotu a sarautar Kano
Sanusi II vs Aminu Ado: ’Yan Najeriya sun bayyana ra'ayoyinsu kan hukuncin kotu a Kano. Hoto: Sanusi Lamido Sanusi, Aminu Ado Bayero. Asali: Facebook

Hukuncin da kotun ta yi a Kano

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Alkalin kotun, Abdullahi Liman ya bayyana cewa duka matakan da Gwamna Abba Kabir ya dauka ba su da tasiri a yanzu.

'Yan Najeriya da dama sun yi martani mabanbanta kan wannan mataki na kotu inda kowa ke fadin albarkacin bakinsa.

Martanin ƴan Najeriya kan hukuncin a Kano

Legit ta zakulo wasu daga cikin martanin jama'a daga sassan kasar baki daya kan hukuncin kotun:

@Northerner0:

"SLS zai sake rasa kujerarsa kenan a karo na biyu?."

@donpanacio:

"Na fada muku gwamnatin Kano da Majalisar jihar suna bata lokacinsu ne kawai, Alhaji Aminu Ado Bayero shi ne Sarkin Kano, ba za ka tashi kawai ka sauya sarki babu bincike ba, Sanusi kansa an bincike shi kafin cire shi, wannan shi ne doka."

@auwerl_serlies:

"Sanusi ne sarki har yanzu."

@sukairaaj:

"HRH Sanus 1:1 Aminu, za mu je hutun karin lokaci."

@ChurcH94414:

"Ina fatan kuna sane da Ganduje ma ya saba umarnin kotu a shekarar 2015, abin dariya."

@ladoskyabays:

"Shin Babbar Kotun Tarayya tana da ta cewa a wannan lamari? a'a... alkalin kawai yana bata sunan bangaren shari'a ne."

Ƴan sanda sun tura sako a Kano

Kun ji cewa Rundunar ƴan sanda reshen jihar Kano ta roƙi jama'a su zauna lafiya a lokacin da ake dakon hukuncin Babbar Kotun Tarayya kan rigimar sarauta.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da jami'in hulda da jama'a na rundunar ƴan sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa ya fitar a Kano.

Asali: Legit.ng

People are also reading