Home Back

Jamus ta kama masu yi wa Rasha leken asiri

dw.com 2024/5/19
Yan sandan wajen binciken ababen hawa
Yan sandan wajen binciken ababen hawa

Daga cikin zarge-zargen da ake yi wa mutanen biyu akwai kasancewa a matsayin masu yin zagon kasa da kuma lalubo yadda za a dasa ababen fashewa kamar yadda ofishin masu gabatar da karar na Jamus a birnin Kalsruhe suka bayyana.

Har'ila yau Jamus ta gayyaci jakadan Rasha a birnin Berlin bayan kamen don karin bayani.

'Yan sanda sun binciki gidajen mutanen da kuma wuraren ayyukansu.

Rahotanni sun bayyana cewa wadanda ake tuhuman sun rika neman wurare da za a iya kai wa hari ciki har da sansanin sojin Amurka da ke Jamus.

People are also reading