PDP Ta Watsawa Atiku Ƙasa a Ido Kan Hadaka da Kwankwaso, Obi, Ta Yi Alfahari
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
FCT, Abuja - Jam'iyyar PDP ta yi martani kan jita-jitar haɗaka da sauran jam'iyyun adawa a Najeriya.
Jam'iyyar ta nesanta kanta da labarin inda ta ce babu wannan maganar amma kofa a bude take ga duk mai son shigowa.
Wannnan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da sakataren yada labaran jami'yyar, Debo Ologunagba ya fitar a shafin Facebook a yau Laraba 5 ga watan Yuni.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ologunagba ya bayyana yadda mutane ke tururuwa zuwa PDP inda ya ce hakan ya nuna jam'iyyar ce kadai zabin ƴan kasar a yanzu.
"Kwamitin gudanarwa na jam'iyya bayan ganawa ta 58 ya tabbatar da cewa PDP ba ta shirin haɗaka da jam'iyyun adawa."
"Sai dai ta ce a matsayin PDP na jam'iyyar al'umma, kofofinta a bude suke ga ƴan Najeriya da sauran mambobin da suka fice daga cikinta."
"PDP ta kasance jam'iyyar adawa mafi karfi wacce za ta iya cin zabe a Najeriya ba tare da magudi ba."
- Debo Ologunagba
Karin bayani na tafe....
Asali: Legit.ng