"Ba Za Ku Ci Banza Ba": An bukaci Gwamna Ya Binciki Ciyamomi Masu Barin Gado
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Rivers - Kungiya a jihar Rivers ta bukaci Gwamna Siminalayi Fubara ya binciki shugabannin kananan hukumomi masu barin gado.
Kungiyar Rivers Development Foundation (RiDeF) ta ce akwai zargin karkatar da kudi daga asusun ƙananan hukumomi kan shugabannin.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a jiya Juma'a 7 ga watan Yuni, cewar TheCable.
Shugabar kungiyar, Rejoice Okoli ta bukaci Fubara ya kafa kwamitin bincike domin bankado badakalar ciyamomin.
"Kungiyar RiDeF tana kira ga Gwamna Siminalayi Fubara kan zargin badakala a shugabancin kananan hukumomi."
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
"Akwai manyan zarge-zarge kan shugabannin kananan hukumomin jihar masu jiran gado."
"Muna rokon Fubara ya kada kwamitin bincike saboda girman zarge-zarge wanda ya daga hankalin mutanen jihar Rivers."
- Rejoice Okoli
Karin bayani na tafe...
Asali: Legit.ng