Home Back

"Ba Za Ku Ci Banza Ba": An bukaci Gwamna Ya Binciki Ciyamomi Masu Barin Gado

legit.ng 2024/7/7
  • Kungiyar Rivers Development Foundation (RiDeF) ta bukaci Gwamna Sim Fubara ya binciki shugabannin kananan hukumomi
  • Kungiyar ta ce akwai manyan zarge-zarge kan shugabannin kananan hukumomin da ke shirin barin mulki wanda ya shafi asusun jihar
  • Wannan na zuwa ne yayin a bangaren shugabannin kananan hukumomin suka zargi Fubara da rike musu makudan kudi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Rivers - Kungiya a jihar Rivers ta bukaci Gwamna Siminalayi Fubara ya binciki shugabannin kananan hukumomi masu barin gado.

Kungiyar Rivers Development Foundation (RiDeF) ta ce akwai zargin karkatar da kudi daga asusun Ζ™ananan hukumomi kan shugabannin.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a jiya Juma'a 7 ga watan Yuni, cewar TheCable.

Shugabar kungiyar, Rejoice Okoli ta bukaci Fubara ya kafa kwamitin bincike domin bankado badakalar ciyamomin.

"Kungiyar RiDeF tana kira ga Gwamna Siminalayi Fubara kan zargin badakala a shugabancin kananan hukumomi."

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Akwai manyan zarge-zarge kan shugabannin kananan hukumomin jihar masu jiran gado."
"Muna rokon Fubara ya kada kwamitin bincike saboda girman zarge-zarge wanda ya daga hankalin mutanen jihar Rivers."

- Rejoice Okoli

Karin bayani na tafe...

Asali: Legit.ng

People are also reading