Home Back

'Yan adawa sun nemi sakin fursunonin siyasa

dw.com 2024/5/19
Zanga-zangar adawa da gwamnatin Shugaba Kais Saied na Tunisiya
Zanga-zangar adawa da gwamnatin Shugaba Kais Saied na Tunisiya

Jiga-jigan 'yan adawa na Tunisiya a wannan Talata sun bayyana cewa za su shiga zaben shugaban kasa cikin wannan shekara ta 2024 idan Shugaba Kais Saied ya saki fursunonin siyasa a kasar tare da dawo da 'yancin bangaren sharia.

Fiye da 'yan adawa 20 suke garkame a gidan fursuna sakamakon matakan da shugaban ya dauka a shekara ta 2021 lokacin da ya karfafa ikonsa a kasar da ke yankin arewacin nahiyar Afirka. Mutane kalilan suka kada kuri'a a zaben raba gardama game da sabon kundin tsarin mulkin. Lokacin shugaban ya dakatar da majalisar dokoki sannan ya rubuta sabon kundin tsarin mulki. 'Yan adawa a kasar ta Tunisiya sun nuna damuwa kan rashin iya samun zaben gaskiya da adalci duba da halin da kasar ta samu kanta.

People are also reading