Home Back

Ta’addanci na haifar da illa musamman ga mata — Amina Mohammed

premiumtimesng.com 2024/5/7
Mafi yawan mata, mazajen su ke yin sanadiyyar rayukan su –  Amina Mohammed
Amina-mohammed

Mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed, ta jaddada muhimmancin magance matsalolin ta’addanci da tallafa wa al’ummomin da abin ya shafa a fadin Afirka.

Mataimakiyar ta bayyana haka ne a yayin da aka yi wani taro na yaki da ta’addanci da aka gudanar a ranar Litinin a Birnin Tarayya Abuja.

Ofishin Mai Ba Da Shawara kan Harkokin Tsaro (ONSA) tare da hadin gwiwar ofishin yaki da ta’addanci na Majalisar Dinkin Duniya UNOCT ne suka shirya. Taron ya aka yi wa taken ‘Karfafa Hadin Gwiwar Yanki Da Ci Gaban Cibiyoyi Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci a Afirka’.

Amina ta ƙara jaddada illar ta’addanci da munanan illolin da yake haifarwa ga al’umma, musamman mata da ‘yan mata waxanda galibi su ne irin ke fuskantar cin zarafi A wannan ta’addanci.

Bugu da kari, ta yaba wa Najeriya bisa kiran taron kolin don magance matsalolin mata, masu rauni, da wadanda ta’addanci ya shafa.

“Dole ne mu samar da ingantattun dabaru da za su magance wadannan kalubale, tare da mai da hankali kan halin da mata da ‘yan mata ke ciki wadanda rashin tsaro ya shafa,” in ji ta.

Da take bayyana muhimmancin saka hannun jari ga matasa, Amina ta bukaci kasashen Afirka da su samar da yanayi mai kyau don ci gabansu da wadata.

Ta kara da cewa muhimmancin taron ya wuce Najeriya, inda ta yi kira da a yi kokarin hadin gwiwa daga kasashen Afirka a fadin nahiyar, ciki har da Ghana da Togo, domin samun ci gaba mai ma’ana wajen yakar ta’addanci da kuma tallafa wa al’ummar da abin ya shafa.

A halin da ake ciki, mataimakiyar babban sakataren ta bayyana takaicinta da damuwa game da yadda ake yin watsi da al’amuran mata da ‘yan mata a manyan tarurrukan duniya.

“A manyan tarukan da shugabannin kasashen duniya ke tattaunawa, an mayar da hankali ne bisa karfafa gwiwar matasa da matakan yaki da ta’addanci, tare da kawar da matsalolin da suka shafi mata.

“Sai dai a yanzu, abin farin ciki ne ganin yadda al’amuran mata ke samun karbuwa a irin wadannan dandali,” in ji ta.

People are also reading