Home Back

‘Maido Tallafin Fetur’: Ahmad Gumi Ya Fadi Abin da Zai Kawo Karshen Zanga Zanga

legit.ng 2024/10/5
  • Zanga zangar adawa da tsadar rayuwa ta shiga kwana na shida inda aka rika samun canje canje kan yadda take gudana
  • Shahararren malamin addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya yi magana kan tallafin fetur
  • A baya Sheikh Ahmad Abubakar Gumi ya yi kira ga matasan Najeriya kan kaucewa zanga zangar saboda wasu dalilai

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kaduna - Shahararren malamin addinin Musulunci a Najeriya Sheikh Ahmad Gumi ya kara magana kan dawo da tallafin man fetur a Najeriya.

Sheikh Ahmad Mahmud Gumi ya yi magana ne kan yadda zanga zangar adawa da tsadar rayuwa ke cigaba a fadin Najeriya.

Sheikh Gumi
Sheikh Gumi ya yi maganar dawo da tallafin mai. Hoto: Dr Ahmad Abubakar Mahmud Gumi Asali: Twitter

Malamin ya ba shugaba Bola Tinubu shawara kan abin da ya kamata ya yi wajen dawo da tallafi a cikin sakon da ya wallafa a Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gumi: 'Dawo da tallafin mai ne mafita'

Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya wallafa cewa dawo da tallafin mai ne mafita ga halin da ake ciki a Najeriya.

Malamin ya ce mutane a Najeriya sun kudurta cewa ba wani abu da zai kawo musu sauki sai dawo da tallafi saboda haka ya kamata gwamnati ta sauraresu.

Gumi ya fadi matakan dawo da tallafin mai

Sheikh Gumi ya ba shugaba Bola Tinubu shawarar dawo da tallafin man fetur na wucin gadi domin saukaka rayuwa.

Ya ce ya kamata a dawo da tallafi na akalla wata shida kafin tsare tsaren da gwamnati ta ce tana yi su fara aiki.

Daukan darasi daga wasu ƙasashe waje

Babban malamin ya ce ya kamata gwamnatin tarayya da duba abubuwan da suka faru a ƙasashen Kenya da Bangladesh domin kaucewa irinsu a Najeriya.

Saboda haka ya buƙaci hukumomin Najeriya da samar da mafita kan halin da ake ciki na tsananin rayuwa da gaggawa domin tsayar da zanga zanga.

Tinubu ya yi magana kan tallafin mai

A wani rahoton, kun ji cewa matasan Najeriya sun fara zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a ranar 1 ga watan Agusta a jihohin ƙasar nan.

Gwamnatin tarayya ta yanke matsaya kan maganar dawo da tallafin man fetur da matasan ke buƙata shugaba Bola Tinubu ya yi.

Asali: Legit.ng

People are also reading