EFCC Ta Dauko Binciken Kwankwaso Ana Cikin Rikicin Masarautar Kano
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Hukumar EFCC ta fara bincike kan zargin karkatar da kuɗaɗen yaƙin neman zaɓen jam'iyyar NNPP ƙarƙashin kwamitin gudanarwa na jam'iyyar da Rabiu Musa Kwankwaso ke jagoranta.
Zargin ya kuma haɗa da rashin biyan wakilan jam'iyyar kuɗaɗensu saboda aikin da suka yiwa jam'iyyar a lokacin zaɓen shugaban ƙasa da gwamnoni a shekarar 2023.
Jaridar Vanguard ta kawo rahoto cewa hukumar EFCC ta gayyaci sakataren jam'iyyar na ƙasa, Oginni Olaposi Sunday, domin tabbatar da zarge-zargen da ake yi a kan Kwankwaso da sakatariyarsa ta musamman Folashade Aliu.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Da yake tabbatar da lamarin yayin wata hira ta wayar tarho da jaridar, Olaposi Oginni ya bayyana cewa ya halarci hedkwatar hukumar EFCC da ke Abuja ranar Laraba ta makon da ya gabata.
Ya ce ya je hedkwatar hukumar ne domin ya yi ƙarin bayani kan ƙorafin da ya shigar a madadin jam'iyyar kan cewa Kwankwaso da tawagarsa sun karkatar da N2.5bn na jam'iyyar.
"Eh tabbas EFCC ta gayyace ni. Na amsa gayyatar kuma na gamsu da sanin makamar aikin jami'an EFCC. Na amsa tambayoyi kan ƙorafin da na shigar a madadin NNPP ba tare da wata tsangwama ko muzgunawa ba.
"Suna so su samu tabbaci cewa zarge-zargen da gaske ne sannan ba domin wata mummunar manufa aka yi su ba."
- Oginni Olaposi Sunday
Yaushe EFCC za ta gayyaci Kwankwaso?
Duba da tabbacin gayyatar da EFCC ta yi wa sakataren jam'iyyar NNPP na ƙasa, a bayyane yake cewa an fara bincike kan ƙarar da aka shigar a kan Rabiu Musa Kwankwaso.
Hakan na nufin nan ba da jimawa ba hukumar za ta gayyace shi domin ya kare kansa daga zarge-zargen.
A wani labarin kuma, kun ji cewa Jagoran NNPP na ƙasa kuma tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya ce bai sa baki a mayar da Sarki Muhammadu Sanusi II kan karaga ba.
Tsohon gwamnan na Kano ya ce nan kusa zai koma Kano kuma zai gano yadda aka yi aka mayar da Khalifan Tijjaniya kan mulki.
Asali: Legit.ng