Home Back

Mu yi wa ƴan Najeriya adalci mu kawo musu sauƙi – Tambuwal

bbc.com 2024/10/5

Mu yi wa ƴan Najeriya adalci mu kawo musu sauƙi – Tambuwal

Mintuna 5 da suka wuce

Wani jigo a babbar jam'iyyar adawar Najeriya wato PDP, ya ce a ganinsa har yanzu gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ba ta ɗauki hanyar gyara ba kan halin matsin rayuwar da ake fama da shi a ƙasar.

Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya ce: "Ni a nawa ra'ayi, har yanzu gwamnatin Bola Tinubu, ba ta ma kama hanya ta yadda za ta shawo kan waɗannan matsaloli musamman na tattalin arziƙi na Najeriya ba, ballantana har a ce ta yi nasara".

Ya ce halin da ake ciki a Najeriya, yana buƙatar gwamnati da jagororin siyasa irinsa, su yi wa jama’a adalci a kawo sauƙin rayuwa.

"Mahi yawancin ƴan Najeriya ba su yi tsammanin za su shiga halin da suke ciki yanzu ba."

Yana wannan jawabi ne a wani ɓangare na jerin hirarraki da ƙusoshin siyasar Najeriya, da muke kawo muku, albarkacin cikar mulkin dimokraɗiyyar ƙasar shekara 25 babu katsewa a karon farko na tarihin ƙasar.

Tsohon gwamnan na Sokoto ya ce halin matsin rayuwar da ake fuskanta a ƙasar, wani babban cikas ne ga mulkin dimokraɗiyya.

A cewarsa, mulkin dimokraɗiyya ya kawo ci gaba a Najeriya musamman idan an aka yi la'akari da taka wa wani tsohon shugaban ƙasar burki lokacin da ya yi yunƙurin tazarce a ƙarshen wa'adinsa na biyu.

Ya ce hatta zaɓen shekara ta 2015, lokacin da ƴan adawa a ƙarƙashin jagorancin Muhammadu Buhari, ya kayar da shugaban Najeriya mai ci a wan chan lokaci Goodluck Jonathan, babban ci gaba ne ga ƙasar.

Kalli wannan bidiyo a sama don ganin cikakkiyar wannan hira.

People are also reading