"Yadda Abba Yayi Abin da ba a Taba Gani a Tarihin Jihar Kano" Inji Hadimin Gwamna
Kano - Hassan Sani Tukur ya zanta da jaridar Legit inda mu ka tattauna da shi game da wasu manufofin gwamna Abba Kabir Yusuf.
Malam Hassan Sani Tukur babban mai taimakawa gwamnan Kano ne a harkokin sadarwa na zamani, a shekarar bara aka nada shi.
Hadimin gwamnan ya bayyana mana cewa a gwamnatinsu ta Kwankwasiyya, babu abin da suka sa a gaba kamar harkar ilmi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A cewarsa, sun lura babu abin da yake maida maras shi ya zama mai shi, talaka ya zama mai hali kamar samun ilmi na zamani.
"Mu a wurinmu harka ta ilmi ita ce ta daya, ta biyu kuma ta uku."
"Dalili kuwa mu na da fahimta cewa ta hanyar ilmi ne wanda ba ‘dan kowa ba zai taka ya zama wani."
- Hassan Sani Tukur
Saboda haka ya ce gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta ware 29% ga ilmi a kasafin kudin 2024 kamar yadda jaridar Vanguard ta kawo.
A hirarmu da shi, Tukur ya ce wannan kudi wanda ya kai N120bn zai taimaka sosai wajen dawo da martaba da kimar ilmi a Kano.
UNESCO ta na ba da shawarar a rika kashe akalla 15% domin ilmi a Najeriya, Premium Times ta taba yin bincike kan haka.
Daga makudan kudin da aka ware za a gyara aji tare da gina wasu sababbi a makarantun firamare da sakandaren gwamnati a jihar.
Hassan ya ce gwamnatinsu za ta samar da kujeru domin jin dadin daukar karatu a Kano, wannan kokari zai shafi aji kimanin 29, 000.
A bangaren jin dadi da kula da malamai, an kawo tsaarin da za a rika ba su bashin kudi a yanzu da ake cikin matsin tattalin arziki.
Akwai malaman BESDA da aka ba aikin gwamnati kuma za a sake daukar wasu.
“Wadannan tsare-tsare ne da za a yi su, kuma za a ba su muhimmanci sosai domin a yi gaggawar magance kalubalen nan.”
“Abin da wannan yake nufi shi ne, za a kula da dawainiyar malamai, ginin makarantu, kayan aiki da kayan ‘yan makaranta.”
A baya an ji cewa shekara guda bayan shiga ofis, Mai girma gwamnan Kano ya ayyana dokar ta-baci domin gyara harkar ilmi.
Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin cew zai kokarin bunkasa ilmi a lokacin da yake kokarin zama gwamnan jihar Kano a zaben 2023.
Asali: Legit.ng