Home Back

Hajjin Bana: Zafi Ya Yi Ajalin Mahajjatan Jordan 14 A Saudiyya

leadership.ng 2024/7/2
Hajjin Bana: Zafi Ya Yi Ajalin Mahajjatan Jordan 14 A Saudiyya
A man effected by the scorching heat is helped by others as Muslim pilgrims arrive to perform the symbolic 'stoning of the devil' ritual as part of the hajj pilgrimage in Mina, near Saudi Arabia's holy city of Mecca, on June 16, 2024. Pilgrims perform the last major ritual of the hajj, the "stoning of the devil", in western Saudi Arabia on June 16, as Muslims the world over celebrate the Eid al-Adha holiday. (Photo by Fadel Senna / AFP)

Akalla mahajjatan kasar Jordan 14 ne suka mutu sakamakon tsananin zafi a kasar Saudiyya, kamar yadda hukumomin kasar suka bayyana.

Ministan harkokin wajen kasar Jordan ne, ya bayyana cewa hakan cikin wata sanarwa.

“14 daga cikin ‘yan kasarmu sun mutu sakamakon yanayin zafi wanda ya kasance mai muni mutuka.”

Ministan ya kuma bayyana cewa har yanzu mutane 17 ba a san inda suke ba.

Sanarwar ta kuma ce ana ci gaba da kokarin gano mutanen da suka bata.

Bugu da kari, kamfanin dillancin labarai na AFP da kungiyar agaji ta Iran sun tabbatar da mutuwar wasu ‘yan Iran biyar, ko da yake ba a bayyana halin da suke ciki ba.

People are also reading