Home Back

Jamus za ta rufe sananin sojinta da ke Jamhuriyar Nijar

dw.com 2024/10/5
Hoto: Carsten Hoffmann/dpa/picture alliance

Gwamnatin Jamus za ta sarayar da sananin sojin samanta da ke birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, bayan da kasashen biyu suka gaza cimma matsaya kan ikon 'yancin aiki da kariya ga sojojin Jamus din.

Ma'aikatar harkokin tsaron Jamus ta ce za ta rufe sansanin a ranar 31 ga watan Agusta mai kamawa, kuma dakarunta za su dawo gida, kamar yadda ta shaidawa majalisar dokokin kasar a birnin Berlin.

Sansanin dai na zama wata tunga ta yakar ayyukan ta'addanci a kasashen yankin Sahel, karkashin kulawar Majalisar Dinkin Duniya, to amma sun gaza cimma matsaya kan tsarin bayar da horo da kuma makamai.

People are also reading