Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fadi Jihohin da Za Su Fuskanci Barazana Sosai
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Nigeria - Yayin da damunar bana ta kankama, gwamantin tarayya ta yi gargadi kan ambaliyar ruwa.
Gwamnatin tarayya ta fadi jihohi 19 inda ake hasashen za a samu ambaliyar ruwa mai muni a Najeriya.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ministan ruwa da tsaftar muhalli, Farfesa Joseph Utsev ne ya bayyana haka a yau Alhamis.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Farfesa Joseph Utsev ya bayyana cewa a karshen watan Yuli da muke ciki za a samu ambaliyar ruwa a jihohi da dama.
Ministan ya ce ambaliyar ruwan na zuwa ne saboda mamakon ruwa da za a rika yi a kwanakin da kuma toshe magudanar ruwa da mutane ke yi.
Ministan ruwa ya lissafa jihohin da za a samu barazanar ambaliyar ruwa sosai a bana. Jihohin su ne:
Ministan ya bayyana cewa ana tsoron ambaliyar ruwa da za samu zai kara ta'azzara cutar kwalara da ake fama da ita a Najeriya, rahoton Radio Nigeria.
Saboda haka ya ce bayan kokarin da gwamnatin tarayya ke yi ya kamata jihohi da kananan hukumomin su kara kokari wajen daukan matakin kariya.
A wani rahoton, kun ji cewa ambaliyar ruwa mai tsananin ƙarfi ta yi sanadiyyar ɓacewar mutane aƙalla 10,000 a gabashin ƙasar Libya.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin dai ya faru ne a sakamakon wata iska mai ƙarfi da ta hankaɗo ruwan teku cikin biranen yankin.
Asali: Legit.ng