Home Back

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

bbc.com 2024/7/3

Rahoto kai-tsaye

Masar da Qatar na shiga tsakani kan yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

..

Asalin hoton, Getty Images

Masar da Qatar sun ce za su ci gaba da ƙoƙarin shiga tsakani kan yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta a zirin Gaza, bayan samun martanin farko a hukumance daga ƙungiyar Hamas kan shirin da kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ke mara wa baya.

Ƙasashen biyu ba su bayar da cikakken bayani kan abun da martanin Hamas ɗin ya ƙunsa ba.

Kakakin ma'aikatar tsaron ƙasar Amurka, John Kirby ya ce ana duba martanin na Hamas. Kungiyar dai ta ce za ta hau teburin sulhu da zuciya ɗaya.

"Mun karɓi maratanin Hamas da ta gabatar ta hannun Qatar da Egypt muna kuma nazartarsa yanzu haka kuma ina tunanin cewar iya abin da za mu iya yi kenan yanzu, tunda mun sami wannan martanin a hannun yanzu, kuma za mu yi aiki a kansa." In ji Kirby.

Wakiliyar BBC ta ce wani jami'in Hamas Aze Tariksh ya ce martanin na su ya bude kofar cimma yarjrjeniya.

To amma wani jami'in Isra'ila da ya nemi a sakaye sunansa ya zargi Hamas da sauya wasu muhimman sassa na daftarin yarjejeniyar, kuma haka a wajensu, tamkar ta yi watsi da yarjejeniyar ne.

People are also reading