Home Back

Turkiyya na son a hukunta masu hannu ga harin Rafah

dw.com 2024/6/30
Hoto: Umit Bektas/REUTERS

Kasar Turkiyya ta lashi takobin yin duk mai yiwuwa wajen ganin an dauki kwakwaran matakai kan firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, bayan farmakin da dakarun Isra'ila suka kai a yankin Rafah na kudancin Gaza.

Da yake jawabi a yayin wani taron da ya jagoranta a ranar Litinin, Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya ce Turkiyya ba za ta taba bari mahukuntan Isra'ila da ya kira marasa tausayi su sha kan harin na yankin Rafah ba.

A nashi bangare shugaban Faransa Emanneul Macron, da ke ziyarar aiki a kasar Jamus ya yi kakkausar suka ga harin da ya rutsa da fararen hula tare da kiran bangarorin biyu da su dakatar da buta wuta nan take.

People are also reading