Home Back

Mulkin mallaka: Sarkin Ashanti ya baje kolin kayan tarihi

dw.com 2024/5/17
Bikin baje kolin kayan tarin da turawan mulkin mallaka suka wawushe a Ghana
Bikin baje kolin kayan tarin da turawan mulkin mallaka suka wawushe a Ghana

Sarkin Ashanti Otumfuo Osei Tutu II ya tsara bikin baje kolin kayayyakin tarihin ne a fadar Manhyia da ke birnin Kumasi, domin tunawa da dakarun Ashanti da suka kwanta dama a lokacin yaki da mulkin mallaka a 1874.

Tun da farko gidajen adana kayan tarihin Burtaniya ciki har da ''British Museum'' sun amince da mika takubban zinare 32 da wasu kayayyakin na alfarma ga masarautar ta Ashanti.

Tarihin Yaa Nana Asantewaa

Baje kolin kayayyakin na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen Turai da Amurka ciki har da Faransa da Jamus da Portugal ke fuskantar matsin lamba na dawo da kayan tarihin da suka wawushe a lokacin mulkin mallaka.

People are also reading