Home Back

BUK Ta Kori Ɗalibai 29, Ta Dakatar Da 3 Saboda Satar Amsa A Jarrabawa

leadership.ng 2024/8/21
BUK Ta Kori Ɗalibai 29, Ta Dakatar Da 3 Saboda Satar Amsa A Jarrabawa

Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) ta kori ɗalibai 29 da dakatar da wasu uku bayan da aka same su da laifin magudi a jarrabawa a shekarar karatu ta baya. Haka kuma, jami’ar ta dakatar da dalibai uku na tsawon zango ɗaya ko biyu yayin da ta wanke wasu uku daga zargin da ake musu.

A cikin wata sanarwa da Daraktan riƙon Kwarya a sashin shirya Jarrabawa da adana bayanai, Aminu Kurawa ya fitar, kuma aka ba wa jaridar LEADERSHIP, ya shaida cewa ɗalibai daga matakin digiri na farko da kuma na gaba sun kasance cikin wannan hukunci.

People are also reading