Home Back

Majalisar Shura a Iran ta yi watsi da takarar Ahmadinejad

dw.com 2024/6/26
Tsohon shugaban kasar Iran Mahmud Ahmadineschad
Tsohon shugaban kasar Iran Mahmud Ahmadineschad

Matakin Majalisar Shurar ya kara kada gangar siyasar kasar na mutanen da ke kokarin maye gurbin tsohon shugaban kasar marigayi Ebrahim Raisi, wanda ake hasashen shi ne zai maye gurbin jagoran addinin islama na kasar Ayatollah Ali Khamenei.

Majalisar Shurar ta tantance 'yan takarar ne tare da sahaler jagoran addinin Ayatollah Khamenei da wasu shehinnan malamai. Sai dai an yi watsi da takarar mace a zaben tare da amincewa da mutum shida.

Daga cikin 'yan takarar akwai fitaccen janar din sojojin juyin juya halin Iran kuma tsohon Magajin Garin birnin Tehran Mohammed Bagher Qalibaf, wanda ya jagoranci murkushe daliban jami´ar Tehran da suka gudnar da zanga-zangar kin jinin gwamnatin kasar a shekarar 1999.

People are also reading