Tsohon Gwamnan Katsina Ya Watsar da PDP, Ya Rungumi APC Mai Mulki
Abdullah Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Katsina - Tsohon gwamnan jihar Katsina, Barista Ibrahim Shehu Shema ya koma jam'iyyar APC.
Shema ya sauya sheka a yau Alhamis 2 ga watan bayan ga watsar da jam'iyyar PDP mai adawa a jihar.
Tun a watan Agustan shekarar 2023 ne Shema ya yi wata ganawa da shugaban APC, Abdullahi Ganduje kan komawa jami'yyar.
Tsohon gwamnan ya goyi bayan Atiku Abubakar a zaɓen shugaban kasa amma a matakin jiha ya yi jam'iyyar APC inda Dikko Umar Radda ya sanu nasara.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shugaban jam'iyyar APC a jihar da Hon. Hamisu Gambo (Dan-Lawan Katsina) sun halarci taron sauya shekar tsohon gwamnan a karamar hukumar Dutsin-Ma.
Shugaba jam'iyyar APC a gundumar Shema ya bayyana Barista Shema a matsayin jagora nagari.
Karin bayani na tafe ...
Asali: Legit.ng