Home Back

Shugaban Senegal zai sasanta ECOWAS da AES

dw.com 2024/8/22
Ecowas-Treffen in Nigeria | Bola Tinubu
Hoto: Gbemiga Olamikan/AP/dpa/picture alliance

Kungiyar ta ECOWAS ta nemi Shugaba Faye na Senegal da ya shawo kan shugabanni uku da suka yi musu tawaye bayan karbe madafun iko da tsinin bindiga a kasashensu, daga baya kuma suka kafa tasu kungiyar wanda ECOWAS ta ce rarabuwar kawuna da ke tsakanin kasashen yammacin Afirka na zama barazana ga tsaronsu.

A ranar Asabar din da ta gabata ce, shugabannin kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka gudanar da babban taronsu a karon farko karkashin kungiyar AES a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, tare da tabbatar da raba gari da kungiyar ECOWAS.

Shugabannin kasashen ECOWAS a taronsu da ya gudana a ranar Lahadi a birnin Abuja na Najeriya sun sake zaben Shugaba Bola Tinubu a matsayin shugabann kungiyar.

Wannan shi ne karon farko a kusan shekaru 50 da kungiyar ta ECOWAS ke rasa mambobinta a irin wannan siga.

People are also reading