NCAA Ta Fitar da Jerin Jiragen Sama 10 da Gwamnatin Tinubu Ta Hana Tashi a Najeriya
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Nigeria - Hukumar NCAA ta dauki mataki mai tsauri kan wasu kamfanonin jiragen sama masu zaman kansu.
NCAA ta tabbatar da kwace lasisin kamfanonin jiragen bisa karya dokokin aiki da suka rattaba hannu a kai.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kamfanoni guda 10 hukumar NCAA ta dakatar bisa saba dokoki sufuri.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hukumar kula da zirgar zirgar jiragen saman Najeriya (NCAA) ta ce ta dakatar da kamfanonin ne bisa gaza sabunta rajista da ya kamata su yi tun ranar 19 ga Afrilu.
NCAA ta kuma zargi kamfanoni da saɓa ƙa'idar aiki wajen daukar fasinja bayan ba su da hurumin yin haka.
Jaridar Tribune ta ruwato cewa hukumar NCAA ta ayyana kamfanonin da suka saɓa dokar aiki kamar haka:
Hukumar NCAA ta ce za ta cigaba da dukan mataki kan dukkan kamfanin da ya saɓawa dokar sufuri a Najeriya domin tabbatar da tsaro.
Hukumar ta ce tuni ta baza jami'anta a filayen jiragen saman Najeriya domin tabbatar da cewa jirage da aka dakatar ba sa aiki.
A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin Najeriya ta kirkiro sababbin jami'ai domin magance matsalolin tsaro a manyan filayen jiragen sama.
An kaddamar da sababbin jami'an tsaron ne a filin jirgin saman kasa da kasa na Janar Murtala Muhammad a birnin Legas.
Asali: Legit.ng