Kano: Masallata Sun Rasa Ransu Bayan Tirela Ta Bi Kansu Ana Tsaka da Jam'in Juma'a
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Kano - Hukumar kiyaye haduara ta kasa, FRSC ta tabbatar da mutuwar masallata akalla 14 a jihar Kano.
Hukumar ta tabbatar da cewa masallatan sun rasa ransu bayan tirela ta kutsa cikin jam'i a masallacin Juma'a.
Lamarin ya faru ne a garin Imawa da ke karamar hukumar Kura kan hanyar Kano zuwa Kaduna da misalin karfe 1:30 na rana, cewar Daily Trust.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
FRSC ta tabbatar da cewa direban ya gagara shawo kan motar inda ya kutsa kan jama'a a yau Juma'a 28 ga watan Yunin 2024.
Kakakin rundunar reshen jihar Kano, Abdullahi Labaran ya ce an binne tara daga cikin wadanda suka rasu a yau Juma'a da rana.
Labaran ya ce sauran wadanda suka samu raunuka kuma suna ci gaba da karbar kulawa a asibiti.
Ya kara da cewa yanzu haka direban ya gudu ba a san ina yake ba inda ya tura sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasu.
Karin bayani na tafe...
Asali: Legit.ng