Home Back

Niger: An Shiga Dimuwa Bayan ’Yan Bindiga Sun Shammaci Sojoji, Sun Raunata Wasu

legit.ng 2024/7/3
  • Dakarun sojoji sun sake gamuwa da matsala bayan harin 'yan bindiga a karamar hukumar Rafi da ke jihar Niger
  • Lamarin ya faru ne a jiya Litinin 10 ga watan Yuni inda maharan suka shammaci sojojin a sansaninsu
  • Shugaban karamar hukumar, Ayuba Usman Katako ya tabbatar da hakan inda ya ce sojoji biyu sun samu raunuka

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Niger - Akalla sojoji biyu ne suka samu munanan raunuka bayan 'yan bindiga sun farmaki dakarun a jihar Niger.

Maharan sun shammaci sojojin ne a sansaninsu a karamar hukumar Rafi da ke jihar a jiya Litinin 10 ga watan Yuni.

'Yan bindiga sun kuma kai farmaki kan dakarun sojoji a Niger
'Yan sun raunata sojoji 2 yayin wani hari a Niger. Asali: Original

Niger: 'Yan bindiga sun farmaki dakarun sojoji

Daily Trust ta tattaro cewa maharan suna kokarin wucewa karamar hukumar Wushishi ne zuwa Mashegu lokacin da suka kai harin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban karamar hukumar Rafi, Alhaji Ayuba Usman Katako ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya nuna damuwa sosai.

Katako ya ce sojojin suna ci gaba da karbar kulawa kuma suna samun sauki a asibitin kwararru na IBB da ke birnin Minna., cewar Punch.

Ya bukaci addu'o'i da kuma goyon baya daga jama'a domin ba jami'an tsaro damar dakile matsalar hare-haren 'yan bindiga.

Niger: 'Yan bindiga sun hallaka mutane 7

A wani labarin, kun ji cewa Aƙalla mutum 7 ne ƴan bindiga suka kashe a wani sabon harin ta'addanci da suka kai a jihar Neja.

Miyagun ƴan bindigan sun kai harin ne a wasu ƙauyukan da ke ƙaramar hukumar Shiroro ta jihar.

Maharan da ake zargin ƴan ta’adda ne sun fille kawunan biyu daga cikin waɗanda lamarin ya shafa, Kabiru Salihu da Abubakar Karaga.

Asali: Legit.ng

People are also reading