Home Back

Masarautun Kano: Kotu Ta Sanya Lokacin Fara Sauraran Shari'ar, Ta Fadi Ka'idar da Za a Bi

legit.ng 2024/7/2
  • Babbar Kotun Tarayya da ke jihar Kano ta shirya fara sauraran shari'ar da aka shigar kan masarautun jihar
  • Kotun ta sanya yau Alhamis 6 ga watan Yuni domin fara sauraran karar wanda aka dage saboda yajin aiki
  • Hakan ya biyo bayan maka Gwamna Abba Kabir a kotu bayan rushe masarautun da gwamnatin Abdullahi Ganduje ta kirkiro

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Kotu ta sanya ranar fara sauraran shari'ar da aka shigar kan rigimar masarautun jihar Kano.

Kotu ta sanya yau Alhamis 06 ga watan Yuni domin sauraren shari'ar ta manhajar Zoom.

Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kano karkashin jagorancin Mai shari'a, A.A Liman za ta fara jin bahasin bangarorin biyu, cewar Aminiya.

Idan baku manta ba, kotun ta sanya Litinin 3 ga watan Yuni a matsayin ranar fara sauraran karar wadda aka dage sakamakon yajin aikin kungiyoyin Kwadago.

Daya daga cikin manyan hakimai a fadar Kano, Sarkin Dawaki Babba, Alh. Aminu Babba Dan Agundi wanda kuma Hakimin Nassarawa ne shi ya shigar da karar a gaban kotun.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dan Agundi yana kalubalantar Majalisar Dokokin jihar da Gwamna Abba Kabir kan rushe masarautun jihar 5 da gwamnatin Ganduje ta kirkiro.

Karin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

People are also reading