Dakarun Sojoji Sun Yi Nasara Kan 'Yan Ta'adda a Jihohin Katsina da Plateau
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Dakarun sojojin Najeriya sun kashe wani ɗan ta’adda a Katsina tare da kuɓutar da wasu mutum biyu da aka yi garkuwa da su a jihar Filato a wani samame daban-daban.
Hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da rundunar sojojin ta fitar a shafinta na X (wanda a baya aka fi sani da Twitter).
Sanarwar ta ce dakarun sojojin tare da tawagar ƴan sanda da jami'an rundunar tsaron jihar Katsina, sun yi artabu da ƴan ta'adda a garin Danmusa hedkwatar ƙaramar hukumar Danmusa a jihar Katsina.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sanarwar ta ce, a yayin ƙazamin artabun da sojoji suka yi da ƴan ta’addan, sun yi nasarar kashe dan ta’adda ɗaya tare da ƙwato bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya, harsasai guda biyu masu kaurin 7.62 mm da kuma babur.
Sojojin sun kuma gano wata jaka ɗauke da jigida guda huɗu da babu komai a ciki da kuma abin caji, wanda ake amfani da shi wajen sadarwa da abubuwa masu fashewa.
A wata arangama ta daban, dakarun sojojin bayan samun kiran gaggawa kan satar mutane a kan hanyar Maraban-Jema’a a ƙaramar hukumar Jos ta Kudu a jihar Plateau, sun ceto mutum biyu da aka sace.
A cewar sanarwar masu garkuwa da mutanen sun tsere ne bayan sun hango sojojin inda suka bar mota ƙirar Peugeot 307 da mutum biyun da suka sace.
A wani labarin kuma, kun ji cewa rundunar sojojin Najeriya tare da haɗin gwiwar jami'an tsaro na farin kaya (DSS) sun hallaka ƴan ta'adda bakwai a jihar Sokoto.
Jami'an tsaron sun samu nasarar hallaka tsagerun ƴan ta'addan ne a yankin Modachi na ƙaramar hukumar Isa ta jihar Sokoto.
Asali: Legit.ng