Home Back

An girka gwamnati a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango

dw.com 2024/7/3
Hoto: TCHANDROU NITANGA/AFP via Getty Images

A wannan Labarar ne Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ta gabatar da sabuwar gwamnati, abin da ya kawo karshen watanni biyar na takaddama bayan sake zaben Shugaba Felix Tshisekedi.

Daga dai cikin mukaman da gwamnatin ta bayyana, har da ministan tsaro da ta sanar da sunan Kabombo Muadiamvita.

Sanarwar bude sabon babin na gwamnati a Kwangon, na zuwa ne kasa da makonni biyu da sanarwar sojoji na murkushe wani yunkuri na kifar da gwamnati.

Sojojin sun yi ikirarin cewa wasu dauke da makamai sun tinkari gidan wani minista kafin daga bisani suka shiga fadar Shugaba Tshisekedi da ke a Kinshasa babban birnin kasar.

People are also reading