"Na Yi Kuka": Hadimin Buhari Ya Fadi Abin da Ya Faru Bayan Tsohon Shugaban Ya Nemi Su Yi Aiki Yare
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Oyo - Tsohon hadimin Muhammadu Buhari, Femi Adesina ya magantu kan yadda ya karbi mukami a gwamnati.
Adesina ya ce lokacin da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bukaci su yi aiki tare ya yi kuka sosai.
Tsohon hadimin ya bayyana haka ne a yau Asabar 22 ga watan Yunin 2024 a Ibadan da ke jihar Oyo yayin karatun littafinsa 'Working with Buhari', cewar Tribune.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce yaji wani iri a lokacin saboda zai bar babban editan jaridar The Sun zuwa wani layi da bai sani ba.
"Mene zan tarar a can? Idan ba na son aikin fa, ko ba na son barin aiki na?."
"Sai dai na yi latti, kuma ina son Buhari, kuma ina son yin aiki da shi matuka."
Adesina ya ce ya dade yana tallata Buhari tun 2003, inda ya ce ana biyansa kudi wanda bai kai abin da ya ke samu kaso daya cikin uku ba a matsayin babban editan The Sun.
Ya ce abin alfahari ne yin aiki tare da Buhari kuma ya buga littafin domin kawar da tunanin da ake yi kan tsohon shugaban kasar.
Kun ji cewa Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura.
Atiku yana tare da tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal a yayin ganawarsu da Buhari.
Asali: Legit.ng