Home Back

Atiku Ya Dauki Zafi Kan Gori da Ake Masa, Ya Fadi Yadda Ta Ceto Siyasar Tinubu a Najeriya

legit.ng 2024/6/26
  • Atiku Abubakar ya magantu kan gorin da ake masa kan taimakonsa da Bola Tinubu ya yi a siyasar Najeriya
  • Ɗan takarar shugaban kasar ya ce babu kamshin gaskiya a maganar da ake yadawa tsakaninsa da Tinubu
  • Ya ce shi ne ma ya kawowa Tinubu dauki a siyasa wanda idan da bai yi hakan ba da Bola bai kawo war haka a siyasa ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana yadda ya taimaki Bola Tinubu a siyasa.

Atiku ya ce idan da bai taimaki Tinubu ba da siyasarsa ta zo karshe kuma da bai kai war haka ba.

Dan takarar shugaban kasar ya bayyana haka yayin da ya ke martani kan cewa Tinubu ya taimake shi a siyasa.

Ya ce babu inda Tinubu ya kawo masa ɗauki lokacin takun-saka da Olusegun Obasanjo kamar yadda ake yadawa.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadiminsa a bangaren yada labarai, Paul Ibe ya fitar a yau Lahadi 9 ga watan Yuni a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ibe ya ce mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya yi kuskure da ya ce Tinubu ya agazawa Atiku lokacin da ya ke shan matsi a PDP.

Karin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

People are also reading