Home Back

GUGUWAR SABON YAJIN AIKI: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce ba za ta amince Gwamnati ta ƙara ‘yan dubunnai kan Naira 60,000 da ta yi ba

premiumtimesng.com 2024/6/26
RAƊAƊIN CIRE TALLAFIN FETUR: ‘Yanzu ƙaramin albashin Naira 30,000 ko tankin Keke NAPEP ba zai cika ba’ – Shugaban NLC

Yayin da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bai wa Ministan Harkokin Kuɗaɗe umarnin sa’o’i 48 ya kai masa ƙarin kuɗin mafi ƙanƙantar albashi domin ya sa hannu, Ƙungiyar Ƙwadago ta TUC ta bayyana cewa ba fa za ta amince a yi ƙarin wasu ‘yan dubunnai a kan Naira 60,000 ɗin da Gwamnatin Tarayya ta ƙara ba, kafin tafiya yajin aiki.

Shugaban Ƙungiyar TUC, Festus Osifo ne ya bayyana haka, ranar Litinin cikin wata tattaunawar da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels.

Ya ce su ba wai sun tsaya lallai sai Naira 494,000 za a biya a matsayin mafi ƙanƙantar albashi ba. “To amma dai gwamnati ta yi wani abin a zo a gani, wanda kowa zai iya cewa ta yi nata ƙoƙarin.” Inji shi.

Da aka tambaye shi adadin da ya kamata gwamnati ta biya matsayin mafi ƙanƙantar albashi sai ya ce, “ya kamata dai kwamitin gwamnatin tarayya ya fito da wani adadi wanda zai tafi kafaɗa da kafaɗa da halin da tattalin arzikin ƙasa da masifar tsadar kayan abincin da ake fuskanta.

“Saboda mun shaida masu ba za mu amince da irin ƙarin Naira 1, Naira 2 ko Naira 3,000 uku kamar yadda ta riƙa yi a baya ba. Sannan daga nan sai ta riƙa alƙawarin da ta san ba iya cikawa za ta yi ba.”

Ya ce ƙarin albashin da za a yi tilas sai ya yi daidai da abin da Naira 30,000 za ta iya saye a 2019 da kuma abin da Naira 18,000 za ta iya saye 2014.

NLC da TUC dai sun bai wa gwamnatin tarayya kwanaki biyar domin a sami tsayayyen farashi, ko kuma su ci gaba da yajin aiki.

People are also reading