Home Back

Babbar Kotu a Kano ta umarci ƴan sanda su fatattaki tsigaggen sarkin Kano Aminu Ado daga fada

premiumtimesng.com 2024/7/2
Gina Jami’oi masu zaman kansu zai sa dalibai samun guraben Karatu – Sarkin Kano, Aminu Bayero

Babbar kotun jihar Kano ta umarci ‘yan sanda da su kori tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero daga fadarsa Nasarawa da yake zaune.

Kotun ta kuma umarci Ado-Bayero da takwarorinsa hudu a Masarautun Bichi, Rano, Gaya da Karaye da su daina bayyana kansu a matsayin sarakuna.

Kotun ta bayar da umarnin ne a ranar Litinin bisa karar da babban mai shari’a na jihar Kano, Kakakin majalisar dokokin jihar Kano, da majalisar suka gabatar a gabatanta.

Idan ba a manta ba, wata babbar kotu a Kano ta dakatar da gwamnatin Abba-Yusuf daga rushe masarautun jihar Kano da kuma naɗa Muhammed Sanusi II sabon sarki.

Sai dai kuma a zaman kotu a Kano eanar Litinin, ta bada umarnin ƴan sanda su kori, Aminu Ado daga gudan sarautan Kano sannan su tabbata baya nuna kansa a matsayin sarki a Kano har sai bayan kotu ta saurari karar da aka shigar a gabanta.

People are also reading