Home Back

Rikici Ya Ɓarke Yayin da Kakakin Majalisa Ya Dakatar da Ƴan Majalisa 3, Bayanai Sun Fito

legit.ng 2024/5/19
  • Shugaban majalisar dokokin jihar Edo, Bƙessing Agbebaku, ya dakatar da ƴan majalisa uku ranar Litinin, 6 ga watan Mayu, 2024
  • Lamarin dai ya haddasa hayaniya a majalisar yayin da waɗanda aka dakatar suka yi fatali da matakin nan take
  • Sun shaidawa kakakin majalisar cewa bai isa ya dakatar da su shi kaɗai ba dole ya bar sauran mambobi su kaɗa kuri'a

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Edo - Kakakin majalisar dokokin jihar Edo, Blessing Agbebaku, na jam'iyyar PDP ya dakatar da ƴan majalisa uku ranar Litinin, 6 ga watan Mayu, 2024.

Rahotanni sun nuna cewa an dakatar da ƴan majalisar ne saboda yunƙurin haifar da fargaba a zauren majalisar ta hanyar amfani da dodo.

Majalisar dokokin jihar Edo.
Rigima ta kaure a majalisar dokokin Edo bayan dakatar da mambobi 3 Hoto: Rt Hon. Blessing Agbebaku Asali: Facebook

Haka zalika an ɗauki matakin dakatar da mambobi uku na majalisar ne bisa zargin sun fara kulla makircin tsige kakakin majalisar da wasu jagorori.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

‘Yan majalisar da aka dakatar sun hada da Donald Okogbe (PDP, Akoko-Edo II), Bright Iyamu (PDP, Orhionmwon II), da Adeh Isibor (APC, Esan ta Arews maso Gabas I).

Shugaban majalisar dokokin jihar Edo, Honorabu Agbebaku ne ya sanar da dakatar da mambobin 3 a zaman yau Litinin, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Mista Agbebaku ya zargi ƴan majalisar da yunƙurin ta da yamutsi a zauren majalisar da ka shirim tsige shugabannin majalisa.

Kakakin ya kuma bayyana cewa wasu mutane sun kawo bokaye zauren majalisar ranar 1 ga watan Mayu, 2024 kuma sun yi tsubbace-tsubbace kana suka bar layoyi a wurin.

Amma wannan dakatarwa ta kawo yamutsi a zauren majalisar domim nan take ƴan majalisar da matakin ya sha suka sa ƙafa suka shure dakatarwar.

A cewarsu:

"Mai girma shugaban majalisa, ba ka da damar dakatar da kowane dan majalisar haka kawai, dole ne sai kowane mamba ya kaɗa kuri'a, ka bar mambobi su kaɗa kuri'a."

Domin kawo ƙarshen tada jijiyoyin wuya tsakanin ƴan majalisar, nan take Agbebaku, ya ɗage zaman majalisar.

A wani labarin

Asali: Legit.ng

People are also reading