Home Back

Mazauna Yankunan Karkarar Sin Sun Samu Karin Kyautatuwar Rayuwa

leadership.ng 2024/4/28
Mazauna Yankunan Karkarar Sin Sun Samu Karin Kyautatuwar Rayuwa

Ma’aikatar noma da raya karkara ta kasar Sin, ta ce Sin ta yi nasarar kyautata yanayin rayuwar mazauna yankunan karkara, inda ta yi nasarar bunkasa kwazon karfafa sassa masu rauni, a fannin samar da ababen more rayuwa a shekarar 2023. Har ila yau, an kaddamar da tsare-tsaren tsaftace muhalli a sama da kaso 95 bisa dari na kauyukan Sin.

Bugu da kari a shekarar 2023, sama da kaso 73 bisa dari na iyalai dake yankunan karkarar Sin na da makewayi mai tsafta, yayin da a daya bangaren kaso sama da 40 bisa dari na gidajen dake yankunan karkarar kasar ke da tsarin sarrafa dagwalon bandakuna. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

 
People are also reading