Home Back

UTME: JAMB Ta Ba Da Umurnin Kamo Iyayen Da Aka Gansu Kusa Da Cibiyoyin Zana Jarabawa

leadership.ng 2024/5/11
UTME: JAMB Ta Ba Da Umurnin Kamo Iyayen Da Aka Gansu Kusa Da Cibiyoyin Zana Jarabawa

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire, JAMB ta umurci jami’an tsaro da duk masu cibiyar zana jarrabawa (CBT) da su cafke duk iyayen da suka gani kusa da cibiyar a lokacin gudanar da jarrabawar ta 2024 (UTME).

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar ta JAMB, Dr. Fabian Benjamin, ya sanya wa hannu a ranar Alhamis, ta ce an bayar da umarnin ne a taron karshe na masu CBT, wanda aka gudanar a ranar Laraba, 17 ga Afrilu, 2024.

JAMB ta bayyana cewa, umarnin ya zama dole biyo bayan kutsawar da wasu iyaye suka yi a lokutan zana jarrabawar da ta gabata.

A cewar magatakardar hukumar ta JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, “duk iyayen da suka ki bin wannan umarnin, ba kawai za a kama su ba ne, za a haramta wa ‘ya’yansu shiga zana jarrabawar.”

People are also reading